Sanarwar da kakakinsa Stephane Dujarric ya fitar jiya, ta ruwaito Antonio Guterres na kuma yabawa da martanin gaggawa da jami'an tsaron kasar suka kai
Sakatare Janar din ya ce MDD, ba za ta taba kaucewa daga ci gaba da bada goyon baya ga al'umma da gwamnatin Somalia ba, a lokacin da suke tsaka da aiki tare domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar.
A ranar Laraba da dadddare ne wasu 'yan bindiga suka farwa gidajen abinci biyu a birnin Mogadishu, inda suka kashe mutane a kalla 17 da raunata wasu 26 tare kuma da yin garkuwa da wasu da ba a san adadinsu ba. (Fa'iza Mustapha)