in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin kiyaye tsaro na Somaliya sun janye daga killacewar da suka yi wa maharan da suka kai hari a wani wurin cin abinci
2017-06-15 20:38:12 cri
Hukumar kiyaye tsaro ta kasar Somalia ta bayyana cewa, sojojin kiyaye tsaro na kasar sun janye daga kawanyar da suka yiwa maharani da suka kai hari a wani dakin cin abinci a Mogadishu, babban birnin kasar bayan da suka harbe dukkan maharan guda shida har lahira.

Kakakin hukumar kiyaye tsaro na kasar shi ne ya bayyana hakan ga 'yan jarida yau. Ya kuma bayyana cewa, game da wadanda aka yi garkuwa da su a sakamakon harin, har yanzu ba a san yawansu da suka mutu ko suka raunata ba.

Rundunar 'yan sandan kasar Somaliya ta sanar da cewa, ya zuwa yanzu harin boma-boman da aka kai a babban birnin kasar, Mogadishu ya haddasa rasuwar mutane a kalla guda 18 tare da raunata mutane 19.

Kungiyar Al Shabaab ta kasar Somaliya ta sanar da daukar alhakin kai wannan hari. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China