in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin IMF da Bankin duniya da WTO sun yi kira da a matse kaimi wajen farfado da harkokin cinikayya
2017-07-07 13:37:55 cri
Shugabar asusun bada lamuni ta duniya IMF da takwarorinta na bankin duniya da hukumar kula da harkokin cinikayya ta duniya WTO, sun yi kira da kasashe mambobin kungiyar G20 su dauki matakan bunkasa harkokin cinikayya.

wata sanarwar hadin gwiwa da shugabannin uku suka fitar, ta ce zurfafa hadin gwiwa a fannin cinikayya tare da samar da dabaru a cikin gida da za su mara masa baya, zai taimaka wajen habaka samun kudin shiga da ci gaba a duniya, tana mai cewa wannan na bukatar shugabannin duniya da za su halarci taron G20 su dauki nagartattun matakai.

Babbar daraktar IMF Christine Lagarde da shugaban Bankin Duniya Jim Yong Kim da darakta janar na WTO Roberto Azevedo, sun ce tun daga farko-farkon shekarun 2000, harkokin cinikayya suka tsaya wuri guda, saboda shingayen cinikayya da suka yi yawa da kuma sauran ka'idoji da ke taimakawa masana'antu na cikin gida kadai tare da kara kirkiro wasu sabbin shingayen. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China