in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na goyon bayan kasancewar EU tsintsiya madaurinki daya
2017-07-05 10:36:27 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping dake ziyara a Jamus, ya gana da shugabar gwamnatin kasar Angela Merkel, inda ya ce kasarsa na goyon bayan kasancewar Tarayyar Turai tsintsiya madaurinki daya.

Shugaban na Sin ya isa Berlin ne a jiya Talata, kuma wannan ita ce ziyararsa ta biyu a Jamus.

Haka zalika, shi ne yada zango na biyu da shugaban ya yi a rangadin aiki da yake a nahiyar Turai, inda ya fara tsayawa a Rasha.

Yayin ziyararsa a Jamus, Shugaba Xi zai je birnin Hamburg don halartar taron kungiyar kasashe masu karfin tattalin arziki wato G20. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China