Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bar birnin Beijing da safiyar yau Litinin zuwa ziyarar aiki a kasashen Rasha da Jamus da kuma halartar taron kasashen G20 karo na 12 a Hamburg.
Shugaba Xi ya amsa goron gayyatar da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin, da shugaban kasar Jamus Frank-Walter Steinmeier da kuma shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel suka yi masa.(Ahmad Fagam)