in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya za ta kaddamar da rigakafin cutar murar dabbobi
2017-07-05 10:10:25 cri
Nan ba da dadewa ba, gwamnatin Nijeriya za ta fara yi wa raguna da tumakai da kuma awaki rigakafi a fadin kasar, domin kare su daga cutar murar dabbobi.

Kwayoyin cuta ne ke haddasawa tare da yada murar wadda ba ta daukar lokaci mai tsawo, a tsakanin tumakai da raguna da awaki, inda suke kamuwa da zazzabi da yoyon hanci da tari da kuma limonia, a wasu lokuta ma ya kan kai ga mutuwa.

Darakta a ma'aikatar harkokin gona da raya karkara na kasar Gideon Mshelbwala ne ya bayyana haka jiya Talata a Abuja, fadar mulkin kasar.

Gideon Mshelbwala, ya kuma tabbatarwa al'ummar kasar kudurin gwamnati na tabbatar da yaki da cutar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China