in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta musanta ikirarin da Boko Haram ta yi na garkuwa da 'yan sanda mata
2017-06-30 11:00:26 cri

Hukumar 'yan sandan Najeriya ta karyata ikirarin da mayakan 'yan tada kayar baya na Boko Haram ta yi na cewar ta yi garkuwa da jami'an 'yan sanda mata 10 a makon jiya a jihar Borno dake arewa masu gabashin kasar.

A wata sanarwa da ta iske kamfanin dillancin labarai na Xinhua a ranar Alhamis ya nuna cewa, mai magana da yawun hukumar 'yan sandan jihar Borno Victor Isuku, ya yi watsi da ikirarin da mayakan suka yi.

A wani faifan bidiyo da wasu jaridun kasar suka bibiya a shafukan internet a ranar Talata, an gano wani mutum dake bayyana kansa a matsayin shugaban Boko Haram Abubakar Shekau, ya bayyana cewa akwai jami'an tsaro mata su 10 dake hannun mayakan 'yan tada kayar bayan.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China