in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya yi tir da harin da aka kai Nijeriya
2017-06-28 09:46:37 cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres ya yi tir da jerin hare-haren bama bamai da aka kai Maiduguri, babban birnin jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya, a ranakun 25 da 26 na watan nan.

Cikin sanarwar da kakakinsa Stephane Dujjaric ya fitar a jiya, Antonio Guterres ya aike da sakon jaje ga al'umma da gwamnatin Nijeriya, inda ya yi wa wadanda suka jikkata fatan samun lafiya cikin gaggawa tare da fatan za a tabbatar da hukunta wadanda ke da hannu wajen kai harin.

Sakatare Janar din ya jadadda goyon bayan MDD ga gwamnatin Nijeriya a yaki da take da 'yan ta'adda da masu tsattsauran ra'ayi.

Rahotanni sun ce 'yan kunar bakin wake sun kai hare-haren bama bamai kan birnin Maiduguri, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 10 tare da jikkata wasu 13. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China