in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta kai hari ga tungar masu tsattsauran ra'ayi a Libya
2017-05-27 13:12:16 cri
Shugaban kasar Masar Abdel-Fattah El-Sisi ya sanar ta gidan telabijin na kasar a jiya Jumma'a cewa, jiragen saman yakin kasar sun kai hari kan tungar masu tsattsauran ra'ayi.Kuma jaridar al-Ahram ta kasar ta ba da labari a shafinta na Internet cewa, tungar na cikin kasar Libya.

Cikin jawabinsa, shugaban Abdel-Fattah El-Sisi, ya ce kasarsa za ta ci gaba da kai hari ga mafakar 'yan ta'adda da wuraren da ake horar da su ba tare da yin wata-wata ba, ko suna cikin harabar kasar ko akasin haka.

Ya kara da cewa Gwamnati ba za ta kyale kashe-kashen da ake yi wa kiristoci Kifdawa na kasar ba.

A cewar jaridar Al-Ahram, alamu sun nuna cewa an kai hari ta sama a cikin kasar Libya, kuma tungar da aka kai wa harin na da alaka da harin da aka kai a kasar Masar kan wasu kiristoci Kifdawa a ranar Alhamis da ta gabata.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China