Babban hafsan sojin kasar Tukur Buratai shi ne ya ya tabbatar da hakan a lokacin gudanar da bikin ranar sojoji na tsawon mako guda inda dakarun Najeriyar suka ayyana muhimman nasarorin da suka cimma a fafutukar da suke yi na murkushe ayyukan ta da kayar baya a kasar.
Ya ce wasu da dama daga cikin mayakan sun mika wuya, wannan ya bayyana a fili cewa dakarun Najeriyar sun karya lagon mayakan Boko Haram a yakin da suke yi da 'ya'yan kungiyar.
Ya ce wannan babbar nasara ce, kasancewar mayakan 'yan ta'addan sun riga sun yanke shawarar mika wuya. (Ahmad Fagam)