in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana yiwa 'yan matan Chibok 82 gwajin lafiya
2017-05-12 12:29:12 cri
Ministar al'amurran mata da jin dadin al'umma ta Najeriya Aisha Alhassan, ta bayyana cewa, 'yan matan makaranta Chibok 82 da aka sako a makon jiya ana yi musu gwajin lafiya domin dawowa hayyacinsu cikin sauri tare da sakin jikinsu a cikin al'umma.

Aisha Alhassan, ta bayyana hakan ne a yayin taron manema labaru a Abuja, babban birnin kasar, tace daga bisani za'a kai 'yan matan wajen bincike game da yanayin tunaninsu.

Ministar tace, tuni aka watsa hotunan 'yan matan 82 domin iyaye su tantance 'ya'yansu kasancewa akwai sunayen dake kamanceceniya da juna.

Aisha ta musanta rahotannin dake cewa ba za'a bar iyayen yaran ganin 'ya'yansu ba, sai dai tace ba kullum ne za'a dinga barin iyayen samun damar ganin 'ya'yan nasu ba.

Haka zalika minister tace gwamnatin Najeriya ba zata yi kasa a gwiwa ba wajen neman maslaha game da yadda za'a sako ragowar 'yan matan na Chibok da ake tsare dasu.

Ta kara da cewa dukkan 'yan matan zasu koma makaranta a watan Satumba ciki har da yara matan 82 na baya bayan nan da aka sako, sannan za'a koya musu sana'o'i.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China