in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban hukumar AU ya yi kira ga kasashe mambobi su cika yarjejeniyar da aka cimma na samar da kudade
2017-06-28 09:33:29 cri
Shugaban hukumar kula da ayyukan Tarayyar Afrika AU Moussa Faki Mahamat, ya yi kira ga kasashe mambobin kungiyar, su yi biyayya ga yarjejeniyar da aka cimma, wanda ya nemi kasashen su bayar da kashi 0.2 na kudaden shiga da suke samu daga kayayyakin da ake shigar da su kasashensu ga Kungiyar.

Moussa Mohamat ya yi kiran ne yayin bude taron kungiyar karo na 29, da aka fara a jiya, wanda kuma zai kai ranar 4 ga watan Yuli.

An cimma yarjejeniyar bada kudin ne tsakanin kasashe mambobin AU yayin taronta karo na 27, wanda ya gudana cikin watan Yulin bara a birnin Kigali na Rwanda, inda ya mai da hankali kan samar da kudaden da kungiyar ke bukata.

Matakin da aka fara amfani da shi a watan Janairun bana, ya umarci dukkan kasashe mambobi su bada kashi 0.2 na haraji kayayyakin da kasashen da ba mambobin kungiyar ba ke shigar da su kasashensu, inda za a iya amfani da shi wajen samar da kudi ga kungiyar.

Manufar AU din ita ce, samar da nagartacciyar hanyar samar da kudade don wanzar da zaman lafiya a nahiyar ta hannun asusunta na wanzar da zaman lafiya, tare kuma da rage dogaro a kan kudaden da take samu daga abokan hulda na kasashen waje. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China