in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya bayyana shawarwari hudu game da ci gaba da aiwatar da 'kasa daya, tsarin mulki biyu' a Hong Kong
2017-07-01 13:52:41 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci bikin murnar cika shekaru 20 da dawowar Hong Kong babban yankin kasar Sin, gami da bikin rantsar da sabuwar gwamnatin Hong Kong da ya gudana da safiyar yau Asabar, inda kuma ya gabatar da muhimmin jawabi.

Xi Jinping ya gabatar da manyan batutuwa hudu game da ci gaba da aiwatar da manufar 'kasa daya da tsare-tsaren siysasa biyu' a yankin Hong Kong.

Da farko, ya ce ya kamata a kara fahimtar dangantaka tsakanin 'kasa daya' da 'tsarin siyasa biyu'. Sannan na biyu shi ne, gudanar da aiki bisa tsarin mulkin kasar Sin gami da babbar dokar yankin Hong Kong.

Sauran batutuwan sun hada da maida hankali kan neman ci gaba da kuma tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Hong Kong.

Xi Jinping ya kara da cewa, ya zama dole a tsaya ga manufar kasar Sin daya tak a duniya. Ya na mai cewa, Sam kasar Sin ba za ta amincewa da duk wani yunkuri na kawo barazana ga ikon mallakar yankinta ba.

Shugaba Xi ya kuma bayyana cewa, dole babban yankin kasar Sin ya kara tallafawa yankin Hong Kong, shi kuma bangaren Hong Kong, ya inganta karfinsa na neman ci gaba da kansa.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China