Xi: za a aiwatar da manufar 'kasa daya da tsare-tsaren siyasa biyu' a yankin Hong Kong ba tare da tarnaki ko tsaiko ba
Shugaban Xi Jingping, ya ce Gwamnatin tsakiya na kasar Sin, za ta tabbatar da aiwatar da manufar 'kasa daya da tsare-tsaren siyasa biyu' ba tare da tangarda ba, kana za ta tabbatar da aiwatar da ita a yankin HongKong ba tare da wani tarnaki ko tsaiko ba.
Shugaba Xi ya yi wannan jawabi ne a yau Asabar, yayin bikin murnar cika Hong Kong shekaru ashirin da dawowa kasar Sin, da kuma bikin kaddamar da gwamnatin musammam na yankin Hong Kong na 5. (Fa'iza Mustapha)