in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na gwamnatin Sin kan harkokin kasashen Afirka ya kai ziyara Kongo Kinshasa
2017-06-30 11:13:24 cri
Daga ranar 27 zuwa 29 ga wata, manzon musamman na gwamnatin kasar Sin kan harkokin kasashen Afirka Xu Jinghu, ya kai ziyarar aiki Kongo Kinshasa, inda ya gana da shugaban kasar Joseph Kabila Kabange, tare da tattaunawa da mataimakin firaministan kasar, kana ministan harkokin waje da bunkasa shiyya shiyya tare.

A yayin ganawar ta su, Xu ya ce, Sin za ta ci gaba da nuna goyon baya ga bunkasuwar kasar Kongo Kinshasa, da karfafa hadin gwiwa irinta moriyar juna a fannonin samar da manyan kayayyakin more rayuwar jama'a, da fannin hakar ma'adinai da makamashi, da raya al'adun bil'adam da sauransu, duka dai da zummar samar da kuzari ga dangantakar abokantaka bisa manyan tsare tsare irinta moriyar juna tsakanin Sin da kasar Kongo Kinshasa.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China