in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fursunoni sun tsere daga gidan kurkuku a gabashin Kongo Kinshasa
2017-06-12 13:12:59 cri
A jiya Lahadi 11 ga wata, an kai hari kan wani gidan kurkuku dake jihar North Kivu a gabashin kasar Kongo Kinshasa, inda fursunoni sama da 900 suka yi tsere. Masu kai harin sun yi musayar wuta da jami'an tsaro, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 11.

Gwamnan jihar North Kivu ya bayyana cewa, baki daya fursunoni 930 ne suka tsere, yayin da masu kula da gidan kurkuku 8 da masu kai harin 3 suka mutu. Ya ce, masu kai hari sun yi amfani da manyan makamai.

Kawo yanzu, ba a gabatar da cikakken rahoto dangane da masu kai harin ba. Bisa labarin da hukumar tsaro ta bayar, an ce, masu adawa da gwamnatin Uganda da masu dauke da makamai farar hula na yankin ne suka aikata wannan danyen aiki.

An labarta cewa, mafi yawan fursunonin da suka tsere daga gidan kurkuku membobi ne na wadannan kungiyoyi biyu. Ana tuhumar su ne da laifin kisan kiyashi kan fararen hula a yankin, har ma wasu ana shari'arsu a halin yanzu. (Fatima Liu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China