in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu ya yi kira ga bangarori daban daban na Kongo Kinshasa da su dakatar da ayyukan nuna karfin tuwo da na harzuka
2016-09-22 10:43:00 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya bayar da sanarwa ta kafofin watsa labaru a jiya ranar 21 ga wata, inda ya nuna damuwa sosai kan rikice-rikicen da suka abku a kwanan baya a wasu wuraren kasar RDC-Congo, ciki har da babban birninta Kinshasa, ya kuma yi kira ga bangarori daban daban da su dakatar da ayyukan nuna karfin tuwo da na harzuka, tare kuma da kawar da bambance-bambance dake kasancewa a tsakaninsu ta hanyar lumana.

A cikin sanarwar, an ce daga rana 19 zuwa ta 20 ga wata, an tayar da rikice-rikicen nuna karfin tuwo tsakanin masu zanga-zanga da jami'an tsaro a birnin Kinshasa da sauran wurare, wadanda suka haddasa rasuwar mutane a kalla 32, ciki har da 'yan sanda guda hudu, dalilin haka, kwamitin sulhu yake nuna damuwa sosai kan lamuran tare da yin allawadai sosai kan miyagun ayyukan da aka yi.

Baya ga haka, kwamitin sulhu ya yi kira ga jam'iyyu daban daban na kasar Kongo Kinshasa da masu goyon bayansu da su dakatar da ayyukan nuna karfin tuwo da na harzuka, tare kuma da kawar da bambance-bambance a tsakaninsu ta hanyar lumana, kana ya kalubalanci jam'iyyu daban daban na kasar da su yi hakuri da hana daukar matakan da za su kara tsanantar da hali, ya kuma kalubalanci gwamnatin kasar da ta yi bincike tare da gurfanar da masu hannu cikin wadannan munanan ayyukan gaban kotu.

A karshe dai kwamitin sulhu ya kara yin kira ga bangarori daban daban na kasar, da su shirya wata tattaunawar siyasa game da batun shirya zaben shugaban kasar yadda ya kamata. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China