in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burundi ta yi bikin cika shekaru 10 da shiga kungiyar EAC
2017-06-29 10:21:31 cri
Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza, ya kaddamar da bikin mako guda na cika shekaru 10 da shigar kasar a kungiyar bunkasa yankin gabashin Afirka ko EAC, matakin da ke taimakawa wajen hade kasar da sauran kasashe na shiyyar.

Kungiyar EAC dai na kunshe da kasashe shida da suka hada da Burundi, da Kenya, da Rwanda, da Tanzania, da Afirka ta kudu da kuma Uganda. Sai dai kuma kawo yanzu, ba ta kai ga zama ta siyasa ba, matakin da shi ne na karshe a matakan dunkulewar kasashen dake cikinta.

Shugaba Nkurunziza, ya bayyana cewa babban kalubalen da EAC ke fuskanta shi ne na hade sassan kungiyar, ta yadda za a kai ga cimma nasarar dunkule kasashen dake karkashin ta wuri guda. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China