in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tanzania ta yi kira ga MDD da ta ci gaba da mara baya ga shirin samar da zaman lafiya a kasashen Burundi da Jamhuriyar Demokradiyyar Congo
2017-03-10 13:44:54 cri
Shugaban kasar Tanzania John Magufuli, ya yi kira ga MDD ta ci gaba da mara baya ga shirin samar da zaman lafiya da tsarin siyasa mai dorewa a kasashen Burundi da Jamhuriyar Demokradiyyar Congo.

John Magufuli ya yi wannan kira ne lokacin da Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres ya yada zango a kasar, a kan hanyarsa ta zuwa birnin New Yorkn daga Kenya.

Shugaban ya ce rashin kwanciyar hankali a kasashen biyu na kara yawan 'yan gudun hijira dake kwarara kasar Tanzania da sauran kasahe makwafta, ya na mai cewa akwai bukatar samar da tsarin siyasa mai dorewa a kasashen.

Ministan harkokin wajen Tanzania Augustine Mahiga da ya gabatar da kiran ga Sakatare Janar na MDD, ya ce a matsayin kasarsa ta jagorar kungiyar kwancen kasashen gabashin Afrika, ta na da kyakkywar fata, la'akari da nasarorin da aka samu a shiga tsakanin rikicin Burundi da tsohon shugaban Tanzaniyar Benjamin Mkapa ya taimakawa samarwa, wanda kuma Shugaban Uganda Yoweri Museveni ya jagoranta. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China