in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe hudu na Afirka sun gayyaci kamfanonin Sin da su zuba jari a kasashensu
2016-02-26 13:45:31 cri
A Jiya Alhamis 25 ga wata, aka fara taron karawa juna sani kan harkokin zuba jari na kasashe guda hudu na Afirka na tsawon kwanaki biyu a birnin Tangshan a lardin Hebei na kasar Sin. Jami'an hukumomin raya harkokin zuba jari da jakadu na kasashen Habasha, Kenya, Mozambique da Zambia sun halarci taron, inda suka gayyaci kamfanonin kasar Sin da su zuba jari a kasashen su.

Jakadan kasar Kenya dake kasar Sin Michael Kinyanjui ya ce, kasar sa ta dauki matakai da dama domin sa kaimi ga kamfanonin kasar Sin da su zuba jari a kasar, bayan kasashen biyu sun daga dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu bisa manyan tsare-tsare. Ayyukan noma da kirkire-kirkire na fuskar makoma mai kyau, kasar tana kuma sa ran raya harkokin masana'antunta.

Kaza lika, a halin yanzu, kamfanonin kasar Sin sama da dubu uku suna zuba jari a nahiyar Afirka, tafiya-tafiyar mutane a tsakanin Sin da Afirka ya kai sama da miliyan 3.6 a shekarar 2014, haka kuma, harkokin da kamfanonin kasar Sin suka zuba jari a Afirka sun hada da makamashi, ma'adinai, kayayyakin gine-gine da dai sauransu, gaba daya sun zuba jari sama da dallar Amurka biliyan 4.7 a nahiyar, lamarin da ya kasance babban bunkasuwar kamfanonin Sin a Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China