Sudan tana fatan Amurka za ta soke takunkumin da ta sa mata kamar yadda aka tsara
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sudan Abdul-Ghani Al-Naeem ya bayyana a jiya cewa, kasarsa na fatan bayan kasar Amurka ta fara aiwatar da shirin hana ci rani, lamarin ba zai kawo barazana ga soke mata takunkumi kamar yadda aka tsara aiwatarwa a hukumance cikin watan Yuli mai zuwa ba.
Bugu da kari, Mr.Naeem ya jaddada cewa, a halin yanzu, akwai hadin gwiwa tsakanin kasashen Sudan da Amurka, kuma ana gudanar da shi cikin yanayi mai kyau, musamman ma a fannonin yaki da ta'addanci, da kuma hana fataucin bil adama.