in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta yi gargadin cewa sabanin tsakanin 'yan tawaye na iya gurgunta tattaunawar sulhu
2017-06-11 13:18:16 cri
Gwamnatin Sudan ta yi gargadin cewa rikicin cikin gida tsakanin 'yan tawayen (SPLM)/ tsagin arewaci zai iya gurgunta shirin tattaunawar sulhu game da batun yankunan kudancin Kordofan da Blue Nile.

Mai Magana da yawun gwamnatin Sudan Ahmed Bilal Osman, shi ne ya bayyyana hakan cikin wata sanarwa, inda ya jaddada aniyar gwamnatin kasar cewa a shirye take ta shiga shirin maido da tattaunawar zaman lafiyar a duk lokacin da masu shiga tsakani na Afrika suka tsayar da lokacin.

Sannan ya bukaci yan tawayen na SPLM/ tsagin arewaci dasu warware sabanin dake tsakainsu, wanda ya bayyana shi a matsayin babban shamaki dake iya kawo cikas game da shirin tattaunawar zaman lafiyar a bangarorin kasar biyu.

A ranar Alhamis ne, majalisar Nuba Mountains Liberation Council wato (NMLC), wanda itace majalisar dokokin SPLM/, ta yanke shawarar tunbuke shugabanta Malik Agar, inda ta maye gurbinsa da tsohon mataimakinsa Abdel Aziz al-Hilu.

Wannan mataki ya zo ne, bayan taron ganawar da NMLC ta shirya, wanda al-Hilu ne ya kira taron.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China