in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sin ya ba da umurni kan aikin ceto a lardin Sichuan
2017-06-24 17:27:59 cri
Da misalin karfe 6 na safiyar yau ne zaftarewar kasa da ta auku a jihar A'ba ta lardin Sichuan dake kudu maso yammacin kasar Sin, hadarin da ya rusa gidaje sama da 40, yayin da ya rufta da mutane sama da dari daya.

Bayan aukuwar zaftarewar kasa a yankin, gwamnatin kasar Sin ta dukufa aikin ceto a wannan yankin, bisa umarnin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayar, wanda ya nemi lardin Sichuan ya dukufa wajen aikin ceton mutanen da suka rufta, domin rage adadin wadanda ka iya rasa rayukansu, da yin rigakafin sake aukuwar iftila'in da kuma kiyaye al'ummar yankin yadda ya kamata.

Bugu da kari, gwamnatin kasar Sin ta aike da tawagar musamman zuwa wurin domin jagorantar aikin ceto da kuma jajantawa al'ummar yankin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China