in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Habasha da Sudan ta Kudu sun yi kira ga kasashen duniya su tallafawa kasashen Afirka masu fama da bala'in fari
2017-02-25 13:06:59 cri
A Jiya Jumma'a ne, firaministan kasar Habasha Hailemariam Desalegn ya gana da shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir, wanda ya ziyarci birnin Addis Ababa, inda shugabannin biyu suka yi kira ga kasashe daban-daban, su samar da tallafin jin-kai ga yankuna masu fama da matsanancin fari a Afirka.

Mista Kiir ya ce, a kasarsa wato Sudan ta Kudu, akwai 'yan gudun hijira da dama da ke bukatar tallafi daga kasashe daban-daban, inda ya ce gwamnatin kasar ba ta da matsala sam, wajen taimakawa hukumomin bada agajin jin-kai gudanar da ayyukansu.

A nasa bangaren, Mista Hailemariam ya nuna cewa, yawan tallafin da kasashe daban-daban suka samar bai isa ba, kuma ya kamata kasashen dake yankin kahon Afirka su inganta hadin-gwiwa ta fuskar tunkarar fari.

A watan Janairun bana, gwamnatin kasar Habasha ta fitar da wani rahoto, inda ta nemi tallafin dala miliyan 950, domin taimakawa 'yan kasar sama da miliyan 5 da matsalar fari ta shafa.

A 'yan shekarun nan, wasu kasashen Afirka na fama da matsanancin fari, ciki har da Habasha, da Sudan ta Kudu, da Kenya, da Somaliya, da Tanzaniya da kuma Uganda.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China