in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 16 sun rasu sakamakon bala'in ambaliyar ruwa a Nijer
2017-06-18 12:55:58 cri
Gwamnatin kasar Nijer ta fidda rahoto a ranar 16 ga wata cewa, cikin makon da ya gabata, an samu ruwan sama mai karfi a kasar, lamarin da ya haddasa bala'in ambaliyar ruwa a wasu yankunan kasar ta Nijer, kuma ya zuwa yanzu, ya riga ya haddasa rasuwar mutane 16, yayin da mutane kimanin 4800 bala'in ya shafa.

Rahoton ya kuma bayyana cewa, an fi fama da bala'in ambaliyar ruwa a babban birnin kasar, watau Niamey, sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi a birnin tun daga daren ranar 13 ga wata zuwa ranar 14 ga wata. Ya zuwa yanzu, bala'in ya riga ya barnata gonaki da dama, kana ya karya wasu gadoji da hanyoyi da ababen more rayuwa da dama.

Haka kuma, Gidan Talebijin din kasar ta Nijer ya daina watsa shirye shiryensa sakamakon ruwan wanda ya shiga babban ginin ofishin Gidan talabijin din.

Bisa kididdigar da ofishin kula da harkokin jin kai na MDD dake kasar Nijer ya fidda a ranar 14, an ce, ruwan sama kamar da bakin kwarya ya haddasa rasuwar mutane 11, ciki har da yara kanana guda 9.

Ministan kula da harkokin jin kai da warware matsalolin da bala'un suka haifa na Nijer Magaji Laouan, ya bayyana cewa, bala'in ambaliyar ruwan ya riga ya rushe gidaje a kalla guda 694, kuma kimanin mutane 4800 ne wannan ibtila'in ya shafa a halin yanzu. Haka kuma, domin fuskantar ibtila'in, gwamnatin jamhuriyar Nijer tana gaggauta ayyukan samar da abinci da kayayyakin agaji ga al'ummomi masu fama da bala'in. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China