Xi wanda kuma shi ne Sakatare Janar na kwamitin tsakiya na Jam'iyyar Kwaminis ta kasar, ya yi kiran ne yayin da yake jawabi a wurin taron kara wa juna sani da ya jagoranta jiya Juma'a a lardin Shanxi dake arewacin kasar Sin, wanda ya mai da hankali kan rage radadin talauci.
Ya ce dole ne a tabbatar da yankuna da mutanen da talauci ya yi wa kaka-gida, sun rayu cikin matsakaicin yanayi tare da sauran al'ummar kasar. (Fa'iza Mustapha)