in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi ya yi bayani game da ziyarar shugaba Xi Jinping a Kazakstan
2017-06-11 13:02:09 cri
Tun daga ranar 7 zuwa 10 ga wannan wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyara a kasar Kazakstan tare da halartar taro na 17 na majalisar shugabannin kasashe membobin kungiyar SCO da bikin bude baje koli na duniya na Astana bisa gayyatar da aka yi masa. Bayan da aka gama wadannan bukukuwa, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi bayani game da ziyarar shugaba Xi Jinping a wannan karo.

Wang Yi ya bayyana cewa, wannan ne ziyara ta farko bayan da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya shugabanci dandalin tattaunawar hadin gwiwar "ziri daya da hanya daya", kana ita ce muhimmiyar ziyarar diplomasiyya ta kasar Sin a yankin Asiya da Turai. A cikin awoyi fiye da 60 da suka wuce, shugaba Xi ya halarci bukukuwa fiye da 20, inda aka tattauna hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Kazakstan, da hangen makomar bunkasuwar kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai tare da halartar bikin baje koli na duniya na Astana. Ziyararsa tana shaida tunanin hanyar siliki wato hadin gwiwa cikin lumana, da bude kofa, da koyi da juna, da samun moriyar juna, da sa kaimi ga inganta "ziri daya da hanya daya" da hada kan juna don shimfida zaman lafiya da samun wadata a yankin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China