in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Zimbabwe: cin hanci babban abun damuwa  nahiyar Afrika
2017-06-24 13:06:27 cri
Mataimakin shugaban kasar Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa ya ce matsalar cin hanci ta zama babbar abun damuwa a Afrika, inda ya ce akwai bukatar magance shi domin tabbatar da bunkasar tattalin arzikin yankin da kuma jan hankalin masu zuba jari na kasashen waje.

Da yake jawabi jiya Jumma'a, yayin wani taro kan huldar kasuwanci tsakanin Afrika ta kudu da Zimbabwe, wanda ya gudana a Johannesburg, Emmerson Mnangagwa ya ce al'ummar Afrika na da matukar muhimmanci a yaki da cin hanci, yana mai kira gare su su hada hannu da gwamnatoci wajen yakarsa.

Ya ce batun cin hanci babbar matsala ce a Afrika, wadda ta damu gwamnati ba kadai a Zimbabwe ba, har ma a nahiyar baki daya.

A bara ne wata kungiyar al'umma ta kasa da kasa mai suna Transparency International ta ruwaito cewa, Zimbabwe na asarar a kalla dalar Amurka biliyan 1 a kowace shekara saboda cin hanci, inda ta bayyana jami'an 'yan sanda da na gwamnati a matsayin manyan masu aikata laifin.

Makasudin taron na yini biyu shi ne, lalubo damarmakin cinikayya da zuba jari da ba a amfani da su, a tsakanin kasashen biyu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China