in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Mugabe ya fara tattaunawa da matasan kasar
2017-06-03 12:13:47 cri
A jiya Juma'a ne shugaba Robert Mugabe na Zimbabwe ya fara wasu jerin tattaunawa da matasan jam'iyyar Zanu-PF mai mulkin kasar gabanin babban zaben kasar na shekarar 2018, zaben da jam'iyyarsa ta tsayar da shi takarar neman shugabancin kasar.

Ana sa ran ganawar farko da shugaban kasar zai yi a Marondera, babban birnin lardin Mashonaland dake gabashin kasar, mai nisan kilomita 80 kudu da Harare, za ta hallara dubban matasa daga lardin da ma nesa, a daidai lokacin da jam'iyyar ke fama da barakar daka iya ba da damar kawar da Mugade mai shekaru 93 daga mulki.

Jaridar The Herald ta ruwaito sakataren matasa na jam'iyyar Kudzai Chipanga yana gargadin duk wasu masu wata manufa baya ga ganawar da shugaba Mugaben zai yi da matasan, da su nisanci taron.

Shugaba Mugabe zai yi tattaki zuwa dukkan lardunan mulkin kasar a lokacin ganawa da matasan, wadanda ake ganin a matsayin kashin bayan nasarar jam'iyyar a zaben dake tafe, biyo bayan takun sakan dake tsakanin Mugabe da wani bangare na tsoffin wadanda suka yi fafutukar kwatar 'yancin kasar. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China