Mr. Yang Sheya, jami'in da ke kula da aikin ya bayyana a jiya Lahadi, cewa za a gama aikin sanya injin samar da wutar lantarki na daban a farkon shekara mai zuwa. Sakamakon haka, injunan biyu za su iya samar da wutar lantarki ga cibiyoyin samar da wutar lantarkin kasar Zimbabwe, ta yadda za a iya magance matsalar karancin wutar lantarki da kasar Zimbabwe take fuskanta.
Mr. Huang Ping, jakadan kasar Sin dake kasar Zimbabwe ya bayyana cewa, wannan aiki zai samar wa kasar Zimbabwe karin wutar lantarki, ta yadda al'ummar kasar za ta samu moriya. (Sanusi Chen)