A yayin da suke madatsar ruwan, jakadun sun yaba da kamfanin na kasar Sin ya kammala aikin cikin sauri da kuma inganci, inda suka yi fatan kasashensu za su kara yin hadin gwiwa da kasar Sin a fannonin samar da makamashi da kayayyakin more rayuwar al'umma.
Jakada Mwana Nanga Mawanmpanga na kasar Kongo Kinshasha dake kasar Zimbabwe ya bayyana cewa, kasar Sin ta kasance abin koyi ga kasashen Afirka wajen neman ci gaba. Kasar Sin na amfani da fasahohinta na zamani wajen samar da kayayyakin more rayuwar al'umma ga kasashen Afirka, domin taimakawa kasashen Afirka wajen neman ci gaba cikin sauri. (Sanusi Chen)