in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin zai halarci taron Davos a Dalian
2017-06-21 19:34:33 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya ce firaministan kasar Sin Li Keqiang, zai gabatar da jawabin bude taron masu ruwa da zaki game da tattalin arziki na Davos, wanda za a gudanar a birnin Dalian dake nan kasar Sin.

Da yake bayyana hakan yayin wani taron manema labarai yau Laraba a nan birnin Beijing, Mr. Geng ya ce za a gudanar da taron ne tsakanin ranekun 26 zuwa 28 ga watan Yunin nan.

Mahalarta taron za su hada da jagorori daga kasashen Finland da Sweden, da wakilai da dama da za su yi musayar yawu game da harkokin cinikayya da na kasuwanci. Kaza lika masana da masu fashin baki tare da 'yan jaridu su ma za su halarci taron.

Taron na bana dai na da taken "samar da ci gaba daga dukkanin fannoni, a yayin sauyi na hudu na ci gaban masana'antu". (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China