Minista Salif Traore ya bayyana cewa, baki daya 'yan yawon shakatawa 4 da soja daya, da kuma 'yan ta'adda 4 sun mutu a sakamakon aukuwar wannan lamari.
A jiya Litinin 19 ga wata, kungiyar masu tsattsauran ra'ayin islama dake da alaka da kungiyar Al-Qaeda, ta yi shelar daukar alhakin tsarawa tare kuma da gudanar da wannan danyen aiki a wata tashar yanar gizo.
An dai kafa wannan kungiya ce a watan Maris na shekarar bana. (Fatima)