in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya yi Tir da harin da aka kai kan jami'an wanzar da zaman lafiya a Mali
2017-06-10 12:04:27 cri
Sakataren Janar na MDD Antonio Guterres, ya yi tir da harin da aka kai kan jami'an wanzar da zaman lafiya na MDD a Mali, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar jami'ai uku.

Cikin wata sanarwa da kakakinsa ya fitar a jiya Juma'a, Sakatare Janar din ya ce harin da aka kai wa jami'an a birnin Kidal ka iya zama laifin yaki, inda ya yi kira da a tabbatar da hukunta wadanda ke da hannu.

Antonio Guterres ya kuma jadadda goyon bayan MDD wajen aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya a kasar ta yankin yammacin Afrika, yana mai jajajantawa iyalan wadanda suka mutu tare da yi wa wadanda suka ji rauni fatan samun lafiya cikin gaggawa.

A cewar Shirin wanzar da zaman lafiya na MINUSMA, an farwa sansaninsa dake birnin Kidal a ranar Alhamis da ta gabata, inda aka yi ta harbi da makaman roka, kuma bayanan farko-farko na cewa gomman kwanson bama-bamai iri daban daban ne aka harba sansanin.

Jim kadan bayan nan ne kuma, aka farwa jami'ai dake wajen sansanin, al'amarin da ya yi sanadin raunatar 8 daga cikinsu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China