in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar 'yan sanda Nijeriya ta musanta rahoton sace mutane 20 a Jihar Kaduna
2017-06-10 12:56:26 cri
Rundunar 'yan sandan Jihar Kaduna dake arewacin Nijeriya, ta musanta wani rahoton dake cewa, an sace mutane 20 ranar Laraba a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Kwamishinan 'yan sandan jihar Agyole Abeh, ya shaidawa wani taron manema labarai a Kaduna cewa, rahoton karya ne tsagwaronsa, da ke neman jefa tsoro a zukatan al'umma.

Agyole Abeh ya ce rahoto da rundunar ta samu a baya-bayan nan shi ne wanda aka tare wasu mutane 5 akan hanyar Kaduna zuwa Abuja, inda aka yi wa 3 daga cikinsu fashi tare kuma da sace wasu guda biyu.

Kwamishinan ya ce babu yadda za a yi a sace mutane 20 dake tafiya tare a mota guda, ba tare da sanin inda aka yi da su ko kuma samun rahoto daga iyalansu ko shaidun gani da ido ba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China