in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Nijeriya ta yi gargadi game da masu kutsen kafar intanet
2017-05-20 13:04:10 cri
Gwamnatin Nijeriya ta yi kira ga masu ruwa da tsaki su yi taka-tsantsan saboda ayyukan masu kutsen intanet, inda ta yi gargadin cewa ana amfani da wata manhaja dake kulle kumfuta har sai an biya kudin fansa da kuma sauran nau'o'in kutse a kasar dake yammacin Afrika.

Mistan harkokin sadarwa na kasar Adebayo Shittu, ya fadawa manema labarai a jiya Juma'a cewa, dole ne a hada hannu don magance duk wani nau'in kutsen intanet a kasar, yana mai cewa, daidaikun mutane har ma da ma'aikatu na iya fadawa tarkon masu kutsen.

Ya ce idan aka shiryawa tunkararsu, to illa da za su yi ba za ta yi yawa ba.

Ministan ya ce tunanin cewa gwamnati ce ke da hakkin shiryawa tunkarar matsalar ba daidai ba ne, ya na mai cewa hadin gwiwa shi ne hanya mafi dacewa ta yaki da ko wani irin nau'i na kutsen intanet a kasar, tun da har kasashen da suka ci gaba ma ba su tsira ba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China