Bugu da kari, ya ce, kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta Boko Haram tana kalubalantar yanayin tsaron lardin Diffa kwarai da gaske, haka kuma, wasu kungiyoyin ta'addanci dake kasashe makwabta, kamar su Libya da Mali, sun kawo barazana ga yanayin tsaro a galibin yankunan dake yammacin jamhuriyar Nijer, watau yankin Sahel. Shi ya sa, aka tsai da kudurin tsawaita dokar ta bacin a wadannan yankuna. (Maryam)