in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fararen hula kimanin 900 sun kamu da cutar gubar abinci a gabashin birnin Mosul na Iraki
2017-06-13 10:23:10 cri
A daren jiya Litinin 12 ga wata, wani memban majalisar dokokin kasar Iraki ya bayyana cewa, mutane kimanin 900 dake zaune a wani matsugunin fararen hula dake gabashin birnin Mosul, sun kamu da cutar guba daga abinci.

Zaihid al-Khatoni, memban majalisar dokokin kasar Iraki mai kula da aikin tsugunar da fararen hula ya bayyana wa 'yan jarida cewa, bayan cin abinci, fararen hula kimanin 900 dake matsugunin U2 a Hasan Sham dake gabashin birnin Mosul sun kamu da cutar guban abinci.

Zaihid al-Khatoni ya kara da cewa, an kai fararen hular da suka hadu da wannan larura asibiti domin samun jiyya, kuma mafi yawansu mata ne da tsoffi da kuma yara. Kawo yanzu ana kulawa da su yadda ya kamata, ba a kuma samu rahoton rasa rayuka sakamakon matsalar ba.

Bisa alkaluman da hukumar ba da taimako ta kasar Iraki ta fitar, an ce, yakin kwace birnin Mosul da aka fara daga watan Oktoban bara, ya riga ya tilasawa fararen hula sama da dubu 700 kauracewa gidajensu. Ya zuwa yanzu kuma, ana ci gaba da dauki ba dadi a yammacin birnin na Mosul. (Fatima Liu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China