in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Ghana ya bukaci shugabannin kasashen Afrika su inganta rayuwar matasa
2017-06-13 09:57:18 cri
Shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo ya yi kira ga shugabannin Afrika su inganta rayuwar matasa domin kawo karshen hadarin da suke fadawa lokacin da suke kokarin tsallake tekun Meditereniyan domin zuwa ci rani.

Wata sanarwar da fadar shugaban kasar ta fitar a jiya, ta ruwaito Nana Akufo-Addo na cewa, idan aka ba matasa damar da suke bukata, to za a samu gagarumin ci gaba ta fuskar tattalin arziki cikin kankanin lokaci.

Da yake jawabi ga taron kawancen kungiyar G20 da Afrika dake gudana a Berlin na kasar Jamus, shugaban kasar ta Ghana, ya ce idan aka samar da yanayi mai kyau a Afrika, wanda zai ba matasa damar inganta kwarewarsu, aka kuma horar da su sana'o'in hannu tare da samun ilimin fasahar zamani, to za su bunkasa nahiyar Afrika. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China