Shirley Botchwey da ta bayyana haka a jiya Alhamis, ta kuma yi kira ga shugabannin da masu ruwa da tsaki su mai da hankali wajen ba matasa damar bada gudunmuwarsu ga tabbatar da ci gaba da zaman lafiya da hadin kai.
Ta ce muradin samar da hadin kai a Afrika da shugabbnin a nahiyar ke fafutukar tabbatarwa, na da matukar muhimmanci ga ci gaban nahiyar, saboda muradin zamewar nahiyar tsintsiya madaurinki daya, shi ne ke karfafa dangantaka tsakanin kasashe mambobin tarayyar Afrika.
Ministar na wannan jawabi ne yayin kaddamar da bikin baje kolin hotuna da aka yi a Accra, babban birnin Ghana, a wani bangare na bikin ranar Afrika. (Fa'iza Mustapha)