A jiya Labara Ghana ta fada wani kazamin rashin wutar lantarki na duk kasa, wanda ya jefa al'ummar ta cikin duhu, tun kusan karfe 10 na daren Larabar ya zuwa karfe 6 na safiyar yau Alhamis
Rahotanni sun bayyana cewa, lamarin ya shafi daukacin lardunan kasar 10, kuma hakan na da nasaba da matsalar na'urori da aka fuskanta, kamar dai yadda kamfanin rarraba lantarkin kasar ECG ya tabbatar.(Saminu Alhassan)