in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude makon cinikayya na kasar Sin a Ghana
2017-05-18 19:34:51 cri
A jiya Laraba ne aka bude makon cinikayya na farko na kasar Sin a Accra, babban birnin kasar Ghana. Manufar makon na kwanaki biyu ita ce, samar da yanayin da ya dace ga 'yan kasuwa da masu masana'antrun kasar ta Ghana ta yadda za su ci gajiyar masu samar da kayayyakin na kasar Sin da ke zaune a Ghana.

Rahotanni na nuna cewa, a kalla kamfanonin kasar Sin 50 daga bangarorin masana'antu daban-daban ne suka baje kolin kayayyakinsu, a wani mataki na samar da kafar yin hadin gwiwa da 'yan kasuwan kasar Ghana.

Kasashen Sin da Ghana sun amfana da hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya dake tsakaninsu, tun lokacin da kasashen biyu suka kulla huldar diflomasiya a tsakaninsu shekaru 57 da suka gabata.

A shekarar da ta gabata yawan kudin cinikayya tsakanin kasashen biyu ta kai dala biliyan 5.976

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China