in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya yi kira ga Sinawa dake zaune a ketare da su shiga a dama da su a hadin gwiwar kirkire-kirkire, da tattalin arziki
2017-06-12 20:20:13 cri

Firaminista Li Keqiang na kasar Sin ya yi kira ga daukacin Sinawa dake zauna a kasashe daban-daban na duniya da su shiga a dama da su a shirin hadin gwiwar kasar da ragowa kasashen duniya game da harkokin kirkire-kirkire da tattalin arziki.

Li wanda ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da wakilai a taron majalisar Sinawa 'yan kasuwa da masu masana'antu dake ketare karo na biyu a nan birnin Beijing, ya ce tattalin arzikin kasar Sin yana bunkasa yadda ya kamata kuma gwamnati tana da tabbacin cimma nasarar manufofin bunkasuwa kamar yadda aka tsara a duk shekara.(Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China