in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar kare hakkin bil-Adam ta MDD ta bude zamanta na 35 a Geneva
2017-06-07 11:18:23 cri

A jiya Talata ne, hukumar kare hakkin bil-Adama ta MDD ta yi kiran da a samar da yanayin tattaunawa da ya dace domin tafiyar da harkokin hukumar yadda ya kamata.

Shugaban hukumar Joaquin Alexander Maza Martelli wanda ya yi wannan kiran yayin da yake jawabi a zaman hukumar karo na 35 a hedkwatarta dake birnin Geneve, ya kuma tunatar da cewa, hukumar za ta bi ba'asin dukkan laifukan take hakkin bil-Adama da aka gabatar mata.

Shi ma a nasa jawabin shugaba Tabare Vazquez na kasar Uruguay, ya bayyana cewa, wajibi ne dukkan kasashe su amince, su ba da goyon baya kana su shiga a dama da su a harkokin hukumar ta yadda za a tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China