in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta nemi karin taimakon kudi don tallafawa iyalai dubu 60 na 'yan gudun hijirar Syria
2017-06-07 11:13:02 cri

Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD UNHCR, ta yi gargadin cewa, muddin ba ta samu karin kudade ba, to za ta zaftare adadin iyalai dubu 60, daga cikin wadanda take baiwa tallafi na wata wata na 'yan gudun hijirar Syria dake kasashen Lebanon da Jordan a farkon wata mai kamawa.

Mai magana da yawun hukumar ta UNHCR, ya shedawa manema labarai cewa, wani muhimmin kaso na kudaden da ake bada taimakon ga 'yan gudun hijirar Syria ya samu gibi, kuma ana bukatar karin kudaden ne cikin gaggawa domin kaucewa rage adadin wadanda ke amfana da tallafin ceto rayuwar 'yan gudun hijirar na Syria a watanni hudun na biyu na wannan shekara.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China