in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a warware sabanin dake tsakanin Sin da Indiya kan batun iyaka cikin sauri
2017-06-06 11:06:19 cri
Jiya Litinin, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying, ta bayyana a yayin taron manema labarai cewa, shugabannin kasashen Sin da Indiya sun mai da hankali sosai kan batun iyakar dake tsakanin kasashen biyu, kuma su kan tattauna kan batun a yayin ganawar tasu a kowane karo, inda suka cimma ra'ayi daya cewa, ya dace a warware sabanin dake tsakanin kasashen biyu kan batun kan iyakoki cikin sauri, lamarin dai zai tallafawa al'ummomin kasashen biyu, wanda ya kuma kasance babban burin kasashen biyu.

Kwanan baya, firaministan kasar Indiya Narendra Modi ya bayyana a yayin da yake ziyara a kasar Rasha cewa, ko da akwai sabani a tsakanin Sin da kasarsa kan batun iyakoki a tsakanin kasashen biyu, amma, cikin shekaru 40 da suka gabata, ba a taba yin musayar wuta a tsakanin kasashen biyu ba domin wannan batu.

Dangane da wannan lamari, malama Hua ta nuna cewa, kasar Sin tana maraba matuka kan bayanin da firaminista Narendra Modi ya nuna, a matsayin manyan kasashe guda biyu a duniya, ya kamata a kiyaye bunkasuwar dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasar Indiya cikin himma da kwazo.

Bugu da kari, ta ce, a halin yanzu, kasashen Sin da Indiya sun dukufa wajen warware batun iyaka bisa tsarin ganawar wakilan musamman nasu, a sa'i daya kuma, an dauki matakai da dama domin kiyaye zaman lafiya da zaman karko a yankin iyaka. A nan gaba kuma, kasar Sin da kasar Indiya za su ci gaba da karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu bisa fannoni daban daban domin raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China