Fannonin da wadannan yarjejeniyoyin suka shafa sun hada da layin dogo, hako ma'adinai, ba da ilmi, fasahar sararin samaniya. Sauran sun hada da musayar siyasa da harkokin shiyya-shiyya da dai sauransu.
Kaza lika, a fannin musayar harkokin shiyya-shiyya, kasashen biyu sun kulla dangantakar abokantaka a tsakanin birane guda takwas, watau lardin Sichuan na kasar Sin da lardin Karnataka na kasar Indiya, birnin Chongqiang na kasar Sin da birnin Chennei na kasar Indiya, birnin Qingdao na kasar Sin da birnin Hyderabad na kasar Indiya, da kuma birnin Dunhuang na kasar Sin da birnin Aurangabad na kasar Indiya. (Maryam)