in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 103 sun mutu a sakamakon hadarin jirgin kasa a Uttar Pradesh dake kasar Indiya
2016-11-21 13:41:42 cri
'Yan sandan kasar Indiya sun bayyana a jiya ranar 20 ga wata cewa, wani jirgin kasa ya kauce daga hanyarsa a yankin Pukhrayan na Uttar Pradesh dake kasar a ranar, hadarin da ya haddasa mutuwar mutane a kalla 103, yayin da mutane kimanin 150 sun ji rauni.

Wani babban jami'in hukumar jiragen kasa ta kasar Indiya ya bayyana cewa, yayin da hadarin ya faru, lokacin daddare ne, fasinjoji da dama suna barci, don haka yawan mutane da suka mutu ko raunata ya yi yawa. Yanzu hukumar ta tura ma'aikata da dama wurin domin bada ceto. An riga an gano gawawwaki 91 a wurin, kana an kai mutanen da suka ji raunuka masu tsanani zuwa asibiti.

Firaministan kasar Indiya Narendra Modi ya bayyana ta shafin Twitter cewa, ya nuna jajantawa ga iyalan mutanen da suka mutu a sakamakon hadarin, da kalubalanci hukumomin da abin ya shafa da su yi bincike nan da nan. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China