in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi bikin taya murnar cika shekaru 37 da samun 'yancin kan Zimbabwe
2017-04-19 11:14:31 cri
A ranar 18 ga wata, aka yi bikin murnar cika shekaru 37 da samun 'yancin kan kasar Zimbabwe a babban filin wasa na kasar dake birnin Harare, inda shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe, ya halarci bikin. Ya bayyana cewa, samun 'yancin kan kasar ta Zimbabwe, shi ne tushen zaman lafiya da bunkasuwar tattalin arzikin kasar, kuma yana fatan za a gudanar da zaben shugaban kasar a shekara mai zuwa yadda ya kamata.

Taken bikin a wannan karo shi ne "kyautata yanayin yin ciniki don bunkasa tattalin arziki da zamantakewar al'umma". A gun bikin, shugaba Mugabe ya duba faretin sojojin kasar tare da yin wani jawabi.

Kasar Zimbabwe za ta gudanar da zaben shugaba da majalisar dokoki da kananan gwamnatocin kasar a shekara mai zuwa. Ko da yake ba a tabbatar da lokacin zaben ba, amma jam'iyyu daban daban sun riga sun fara yakin neman zaben.

Kafin hakan, jam'iyyar dake kan karagar mulkin kasar Zimbabwe wato Zanu-PF ta sanar da cewa, shugaban kasar na yanzu Mugabe mai shekaru 93 da haihuwa zai zama 'dan takarar jam'iyyar a zaben shugaban kasar na shekarar 2018. Idan ya cimma nasarar zaben, zai zama shugaban kasar har zuwa lokacin da shekarunsa za su kai 99 a duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China