in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta ce tana mai da hankali wajen dakile ISIS da sauya gwamnatin Syria
2017-04-11 13:16:34 cri
Kakakin fadar shugaban kasar Amurka Sean Spicer, ya bayyana a jiya Litinin cewa, yanzu haka kasar sa na mai da hankali matuka wajen dakile ayyukan kunigyar ISIS ta masu tsattsauran ra'ayin Islama, tare kuma da kokarin sauya gwamnati a kasar Syria.

Bugu da kari, Sean Spicer bai kawar da yiyuwar sake harba mamakamai masu linzami kan dakarun sojin gwamnatin Syria bisa umurnin shugaba Donald Trump ba. Ya kara da bayyana cewa, idan an sake yin amfani da makamai masu guba ko boma-boman man fetur kan fararen hula a kasar Syria, tabbas kasar Amurka za ta mayar da martani. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China